Friday 17th of April 2026
No record found
Labarai / 2026-03-14 16:31:44

Al’ummar Dubai Sun Roki Gwamnati Ta Sanyasu Cikin Tsarin Kwashe Shara a Gombe

Daga Hassan Lawan Koli

Al’ummar anguwar Dubai da ke kewayen garin Gombe sun bayyana damuwarsu kan tarin shara da ke cikin anguwarsu, wanda a cewarsu ya dauki shekaru ba tare da an kwashe shi duka ba.

Mazauna yankin sun ce a baya suna hada kudade a tsakaninsu domin daukar kamfanin kwashe shara mai zaman kansa da zai rika kwashe sharar daga wurin da suka tanada. Sai dai sun ce halin kuncin rayuwa da ake ciki a yanzu ya sa suka kasa ci gaba da biyan kudin wannan aiki.

Saboda haka ne suke rokon gwamnati da ta sanya anguwarsu cikin tsarin kwashe shara na gwamnati domin su samu sauki daga wannan tarin shara, wanda a cewarsu na lalata muhalli tare da jefa lafiyar al’umma cikin hadari, musamman yara da kuma mutanen da ke zaune kusa da wurin zubar da sharar.

A cewar mazauna yankin, wurin tara sharar da ake amfani da shi a yanzu, al’umma ne suka hada kudade suka sayi fili tare da gina shi domin tara sharar da ake samarwa a cikin anguwar.

Sai dai rashin kwashe sharar zuwa babban wurin zubar da shara na gwamnati na ci gaba da damun mazauna yankin, inda suka ce lamarin na iya janyo matsalolin lafiya.

Wani mazaunin yankin, Aliyu Adam, ya bayyana cewa sun dauki matakin gina wurin tara sharar ne bayan sun ga gwamnati na gina irin wadannan wurare a wasu sassan garin Gombe.

“Lokacin da muka ga gwamnati na gina wuraren tara shara a cikin garin Gombe, sai mu ma muka sayi fili muka gina namu da fatan gwamnati za ta kula da shi. Har ma mun fara biyan wani kamfani mai zaman kansa domin kwashe sharar, amma yanzu muna rokon gwamnati da ta amince da shi a matsayin wurin tara shara na hukuma,” in ji shi.

Shi ma wani mazaunin yankin, Abubakar Babadidi, ya ce mutanen da ke zaune kusa da wurin suna fama da wari mai karfi, musamman a lokacin damina.

“Mutanen da ke kusa da wannan wurin tara shara suna shan wahala saboda wari, musamman a lokacin damina, kuma muna tsoron hakan na iya janyo matsalolin lafiya,” in ji shi.

Har ila yau, Abubakar Adamu ya ce a baya jami’an hukumar kula da tsaftar muhalli suna zuwa su kwashe wani bangare na sharar, amma yanzu sun daina zuwa gaba daya.

“A baya jami’an hukumar muhalli suna zuwa su kwashe wani bangare na sharar, amma yanzu sun daina zuwa gaba daya ko da muna rokon su,” in ji shi.

Lamarin ya kuma shafi masu sana’o’i da ke gudanar da kasuwanci kusa da wurin zubar da sharar. ‘Yan kasuwa sun ce wannan yanayi na kazanta na korar masu sayen kayayyakinsu, lamarin da ya sa suke rokon gwamnati da ta dauki matakin gaggawa.

Wani mai sayar da kayan miya a yankin, Dan Gudiri, ya ce wannan matsala ta shafi kasuwancinsa matuka.

“Na rasa kwastomomi da dama saboda ba sa iya jure wannan kazantar muhalli. Wasu kadan suna hakuri suna saya, amma ina rokon gwamnati da ta dauki mataki cikin gaggawa kan wannan matsala,” in ji shi.

Masana harkokin lafiyar al’umma sun gargadi cewa irin wannan tarin shara da ba a kwashewa na iya haifar da gurbacewar muhalli da kuma barkewar cututtuka masu alaka da kazantar muhalli da gurbacewar abinci, musamman a lokacin damina.

Wani masanin lafiyar al’umma, Dr Danimo Mustapha, ya bayyana cewa rashin ingantaccen tsarin kwashe shara na daga cikin manyan abubuwan da ke janyo yaduwar cututtuka masu alaka da muhalli a cikin al’umma.

A halin yanzu, al’ummar yankin na fatan gwamnati za ta tallafa wa kokarinsu na tsawon shekaru wajen tsaftace muhallinsu, ta hanyar sanya anguwarsu cikin jerin wuraren da motocin hukumar tsaftar muhalli za su rika zuwa domin kwashe sharar da ake tarawa a wurin.

342 0

Comments

Leave a comment

Newsletter

Yi rajista domin kasancewa daya daga cikin masu samun labarai da dumi-duminsu daga babban Editanmu

Kayi rajista

Muhimmai

Labarai / 2026-03-14 16:31:44
Al’ummar Dubai Sun
NEWS / 2026-04-02 06:17:40
Gombe Police Officers Dem
NEWS / 2026-03-24 18:06:45
Gombe L-PRES Equips Six U
NEWS / 2026-03-14 16:26:38
Zakat & Waqf Foundati
NEWS / 2026-03-14 16:22:16
Dubai Community Urges Gov

Gombe Reporters

Gombe Reporters is an online channel based in Gombe.....

Quick Links

© Gombe Reporters.. All Rights Reserved.